HASKEN MUSULUNCI
                                
                            
                            
                    
                                
                                
                                February 6, 2025 at 06:59 PM
                               
                            
                        
                            *Assalamu Alaikum*
-
*_29/04/1440,_* _Lahadi._
*_06/01/2019,_* _Lahadi._
-
**
-
*Wallafar:*
Sheikh: Salihu  bn  Fauzan  bin  Abdallahil  Fauzan.
*Fassarar:* 
Aliyu  Muhammad  Sadisu 
*Wanda  ya  duba:* 
Attahiru  Bala  Dukku 
-
*DARASI NA (055)*
*__________________*
-
*_•┈┈┈┈•﷽•┈┈┈┈•_*
-
_Kore  imani  dangane  da  wanda   bai  yi hukunci da abinda Allah  ya  saukarba._
-
_Yana  nuna  cewa  ashe  hukunci  da shari’ar  Allah  imanine  kuma  aƙidace  kuma  bautawa Allah  ne,  wannan  ya  zama  kowanne  musulmi  ya bautawa  Allah  dashi,  ba  wai  za’a  yi  hukunci  da  shari’ar Allah  bane  don  cewa  hukunci  da  ita  shi  ya  fi  yi  wa mutane  kyau kuma shi  ya  fi  tabbatar  da  tsaro  ba._
-
_Domin wasu sun fi maida hankali  akan wannan ɓangaren, sai su bar  ɓangaren  farko._
-
_Kuma  Allah  maɗaukakin  sarki haƙiƙa  ya  aibanta  waɗanda  suke  hukunci  da  shari’ar Allah  domin  fa’idar  kansa  ba  wai  domin  bauta  ga  Allah maɗaukakin  sarki  ba._
-
```Allah mai girma da ɗaukaka yana cewa:```
-
_*(“Kuma  idan  aka  kirayesu  izuwa  ga  Allah  da Manzonsa  domin  ya  yi  hukunci  a  tsakaninsu  kawai  sai wasu  tawaga  daga  cikinsu  su  juya  baya,  idan  kuwa  ya kasance  su  suke  da  gaskiya  sai  su  zo  wurinsa  a  guje”)*_. Suratun  Nur,  aya  ta:  48-49. 
-
_Su  basa  himmatuwa sai  akan abinda suke so, abin kuwa da  ya  saɓawa  son  zuciyarsu  sai  su  kawar  da  kawunansu daga gareshi, domin  su  basa  bautawa  Allah  da  kai  ƙararrakinsu  wurin Manzon  Allah (ﷺ)._ 
-
*Allah ka datar damu.*
*__________________*
_Muhammad bn Umar_
"
DAGA
Zauren *HASKEN MUSULINCI*
"
Ga masu buƙatar shiga zauren sai su aiko da cikakkiyar sallama tareda cikakken suna ta wannan number ɗin ta whatsApp sai su faɗi buƙatar su
+2348133045868
"
Domin samun mu a facebook ɗin mu kuma sai a biyo mu ta wannan koren link ɗin, ta hanyar danna shi. https://mobile.facebook.com/groups/151610345250905?refid=27&ref=opera_speed_dial_freefb
"
سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك