
Sirrin rike miji
June 11, 2025 at 08:37 PM
Wani mutum yazo wajen Manzon Allah (ﷺ) yace : Yah Manzon - Rahma zan tambaye ka rayuwar duniya da ta lahira.
1. Yah Manzon Allah ina son in zama mafi sani a cikin mutane ?
Sai MANON ALLAH yace "Ka ji tsoron Allah ka bi dokokin Sa.
2. Ina son in zama mafi arziki a cikin mutane ?
Manzon Allah ya ce : Ka zama mai wadatar zuci.
3. Ina son na zama Wanda yafi kowa acikin mutane ?
Sai ya ce : Ka zama mai amfanarwa.
4. Menene zai kare ni daga wuta ?
Sai ya ce : Ka zama mai yawan yin Azumi.
5. Ina so in zama mafi adalci a cikin mutane ?
Sai ya ce : Ka so ma d'an uwanka abin da ka ke soma kanka.
6. Ina son in zama mafi amfanin mutane a wajen Allah ?
Sai ya ce : Ka yawaita tuna Allah.
7. Ina son imanina ya zama ingantacce ?
Sai ya ce : Ka gyara halayen ka.
8. Menene yake huce fushin Allah (SWT.) ?
Sai ya ce : Ba da zakka A ɓoye da kyautata wa 'yan uwa.
9. Wani zunubi yafi muni awajen Allah ?
Sai ya ce : Mummunar hali shine rowa
10. Ina so in zama mafi biyayya ga Allah ?
Sai ya ce Ka bi umurnin Allah za ka zama mafi rinjaye a wurin Allah.
Ina roqon Mai karatu dan girman Allah dan son Annabi kayi ƙokari ka tura koda A group 1 ne domin tunasarwa.
Manzon Allah (ﷺ) yace : " Idan Allah ya shiryar da mutum guda ta dalilinka, yafi Alkhairi gareka fiye da abaka jajayen raqumma"
Allah yabamu ikon yin aiki da abinda mukaji . Ameen 🤲
Abu Ahmad Assiddeeq
🙏
❤️
👍
😢
🤲
🥹
22