
Aminiya
279 subscribers
About Aminiya
Sahihin Shafin Jaridar Aminiya. Jaridar Hausa Ta Rukunin Kamfanin Media Trust; Mamallakin Jaridar Daily Trust, Trust TV Da Kuma Trust Radio.
Similar Channels
Swipe to see more
Posts

Hausa da Fulatanci da Yarbanci na cikin jerin harsunan duniya 34 da gwamnatin Saudiyya ta sanar cewa kai-tsaye za gabatar da fassarar huɗubar Ranar Arfa a cikinsu a bana. Karin bayani: https://aminiya.ng/za-a-gabatar-da-hu%c9%97ubar-ranar-arfa-a-harsunan-najeriya-3/

Atiku Abubakar ya zargi gwamnatin Shugaba Tinubu da yin “amfani da talauci a matsayin makami” domin juya ’yan Najeriya. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/gwamnatin-tinubu-na-amfani-da-talauci-a-matsayin-makami-atiku/

“’Yan bindigar sun sace mutane 50, amma yayin da muke ƙoƙarin kai ɗauki, sai muka ga jirgin soji, kuma ya fara harbin mu,” inda ya kashe kimanin mutane 20, in ji wani wani mazaunin yankin Mani a Ƙaramar Hukumar Maru ta Jihar Zamfara. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/jirgin-soji-ya-kashe-yan-sa-kai-20-da-ke-fatattakar-yan-bindiga-a-zamfara/

A karon farko, rundunar tsaron Indiya ta amsa cewa ta rasa wasu jiragen yaƙi a yayin artabunsu da ƙasar Pakistan. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/indiya-ta-amsa-cewa-pakistan-ta-kakka%c9%93o-jiragen-ya%c6%99inta/

Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa shugabancin Najeriya ya faɗa a hannun mutanen da ya kira ‘’yan bindigar birni’. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/yan-bindigar-birni-sun-kar%c9%93e-shugabancin-najeriya-el-rufai/

Mutane tara sun mutu wasu da dama sun jikkata sakamakon fashewar bom da ’yan Boko Haram suka dasa a ƙauyen Mairari da ke Ƙaramar Hukumar Guzamala ta Jihar Borno. Karin bayani: https://aminiya.ng/bom-%c9%97in-boko-haram-ya-kashe-fasinjoji-9-a-tashar-mota-a-borno/


Wani magidanci ya harbe ɗansa mai shekara 15 har lahira a gona bisa kuskure saboda zaton biri ne. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/uba-ya-harbe-%c9%97ansa-bisa-saboda-zaton-biri-ne/

’Yan daban sun ciro Mataimakin Firinsifal daga motar ’yan sanda suka yi masa dukan kawo wuƙa saboda ya hana ɗalibinsa satar jarabawar WAEC. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/an-laka%c9%97a-wa-mataimakin-firinsifal-duka-saboda-hana-satar-a-jarabawa/


Aƙalla mutum 20 ne aka tabbatar sun mutu sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da tawagar Jihar Kano da ke dawowa daga gasar wasannin motsa jiki ta ƙasa (NSF) da aka kammala a Jihar Ogun. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/mutane-20-sun-rasu-a-hatsari-motar-yan-wasan-jihar-kano/

Yawan mamata a ibtila'in ambaliyar da ta auku a Jihar Neja ya ƙaru zuwa mutum 151, a yayin da wasu 3,018 suka rasa muhallansu, ruwan ya shanye al’ummomi uku a Ƙaramar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja. Ƙarin bayani: https://aminiya.ng/mutanen-da-suka-rasu-a-ambaliyar-ruwa-a-neja-sun-%c6%99aru-zuwa-151/