
TRT Afrika Hausa
55.4K subscribers
Verified ChannelAbout TRT Afrika Hausa
Afirka tsantsarta
Similar Channels
Swipe to see more
Posts

A wata sanarwa da kakakin Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya fitar, ya tabbatar da cewa an kuma umarci Salisu Mustapha ya ajiye mukaminsa na Babban Sakatare na Establishment, a ƙarƙashin Ofishin Shugaban Ma’aikata, domin a gudanar da bincike ba tare da tangarɗa ba.👇 https://trt-global.com/afrika-hausa/article/1d8c1f1bfa96


Hukumar tsaro ta farin kaya ta NSCDC reshen jihar Zamfara ta kama lita 1,571 ta man fetur da aka yi fasa ƙwaurinsu kana ake zargin za a kai su wuraren 'yan bindiga a jihar. A yayin zantawarsa da manema labarai a madadin kwamandan NSCDC na jihar, jami'in hulɗa da jama'a rundunar Sani Mustapha ya bayyana cewa an kama wasu mutane huɗu da ake zargi da aikata laifin a wurare biyu daban-daban. Biyu daga cikin wadanda ake zargi, ma'aikatan da ke sayar da mai ne a wani gidan mai, sai kuma sauran biyun an kama su a ƙananan hukumomin Birnin Magaji da Tsafe na jihar.


Sarkin Musulmai na Nijeriya Alhaji Muhammad Sa'ad Abubabakar III ya sanar da ganin watan azumin Ramadana na 2025 a ƙasar a ranar Juma'a. Sarkin ya umarci Musulmai a faɗin ƙasar da su tashi da azumi ranar Asabar 1 ga watan Mayu, wanda ya yi daidai da 1 ga Watan Ramadana na 1446 bayan Hijira.


Minista Sidi Mohamed Raliou ya bayyana cewa "nan ba da jimawa ba za a bayar da shawara game da tsayayyar mafita domin tabbatar da tsari mai tsabta wajen ƙayyade amfani da kafafen sada zumunta a Nijar." https://www.trt-global.com/afrika-hausa/article/67dd06449887

Firaministan ƙasar Habasha Abiy Ahmed da Shugaban Ƙasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamud sun tattauna a kan haɗin gwiwa kan tsaro da kasuwanci sakamakon ƙarfafar da alaƙarsu ta yi.


"Ina ganin Messi na son ya dawo Barcelona. Ya kwashe tsawon shekaru a can. Ƙwarai na tabbata Messi zai dawo, wataƙila a matsayin ɗan wasa, amma na san zai iya komowa a wani matsayin daban... Sunansa da sunan Barcelona abu guda ne. Yana ƙaunar kulob ɗin", cewar Javier Tebas. 👇🏾https://trt-global.com/afrika-hausa/article/7ba7a83daa9b


Shugaban 'yan ta'addar PKK Abdullah Ocalan ya yi kira da a rusa dukkanin kungiyoyin da ke da alaka da PKK, yana mai kira da a kawo karshen ta'addancin da ta shafe shekaru da dama tana yi. 👇🏻 https://www.trtafrika.com/ha/turkey/shugaban-pkk-da-ke-kurkuku-ocalan-ya-yi-kira-da-a-rusa-kungiyar-taaddancin-18269491


Zinari ne abin da ya fi samar wa ƙasar Ghana kuɗin shiga daga ƙasashen waje inda ya ba da gudunmawar da ta kai kashi 53 cikin 100 na kuɗaɗen shigarta. https://www.trtafrika.com/ha/africa/ghana-ta-samu-cedi-biliyan-294-daga-kasuwanci-a-shekarar-2024-18269347

Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) tana neman dala biliyan shida saboda Sudan a wannan shekara daga ƙungiyoyin ba da agaji na duniya don rage wahalar da ake sha a abin da ta kira ɗaya daga mafi munin matsalar da aka fuskanta a duniya, matsalar da take ƙara ƙamari saboda yadda mutane suka barin gidajensu da kuma ƙaruwar yunwa.


Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote Aliko Dangote ya bayyana irin kalubalen da ya fuskanta wajen ganin an cim ma nasara a aikin gina matatar mansa. Hamshakin attajirin ya bayyana hakan ne yayin wata hira da jaridar Forbes ta yi da shi a ranar Linitin, Dangote ya ce aikin gina matatar man shi ne “babban kasadar da ya taba dauka a rayuwarsa’’, inda ya kara da cewa ya kuduri aniyyar samar da tsarin bunkasa masana’antu a fadin Afirka.
